Mun shimfiɗa tubalin magance matsalolin Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya fahimci irin sadaukarwar da iyalai suka yi a shekarun baya-bayan nan inda kuma ya bayyana fatansa na samun ci gaba a Najeriya.

Ya kuma ce har yanzu tsaro na ka gaba a manufofin gwamnatinsa yayin da ƙasar ke ci gaba da tunkarar ƙalubale gadan-gadan kuma ana samun ci gaba yana mai bai wa ƴan Najeriya tabbacin cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin ƴan Najeriya suna harkokinsu ba tare da zullumi ba.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a jawabinsa na bikin shekara uku kan mulki inda ya ce gwamnatinsa ba ta kai ga magance matsalolin ƙasar ba amma sun dasa tubalin samun ci gaba.

Ya ce aikin da ke gabansu shi ne tabbatar da cewa al’ummar Najeriya sun amfana daga sauye-sauyen da gwamnatinsa ke yi.

Shugaban ya kuma ce gwamnatinsa za ta ci gaba da tabbatar da cewa farashin kayan masarufi da ya sauka tun 2023/2024 bai tashi ba.

Ya kuma ce yana aiki don rage kuɗin sufuri kasancewar masu ababen hawa na mayar da motocinsu zuwa masu amfani da iskar gas da motoci masu amfani da lantarki.

Post masu alaƙa

NAHCON ta ɗauki mataki bayan mahajjatan Najeriya sun yi bore kan rashin ingancin abinci

Aminu Abdussalam ne ɗantakararmu na gwamna a 2027 – Kwankwaso

Tsadar kayan abinci ta jefa mu cikin tsaka mai wuya — Mazauna Abuja