Wani sabon rahoton da ƙungiyar kula da yara ta Save the Children ta fitar ya ce aƙalla yara 180 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kwango ne suka rasa uwa da uba ko kuma ɗaukacin masu kula da su sanadiyyar ɓarkewar cutar Ebola tun daga watan Mayu.
Hukumomi a lardin Ituri, inda nan ne cibiyar yaɗuwar cutar sun ce an kuma raba yara sama da 100 sanadiyyar karɓar magani.
Ƙungiyar ta nuna damuwa kan cewa yaran da abin ya shafa na cikin haɗarin fuskantar cin zarafi da kuma shiga cikin damuwa.
A yanzu ƙungiyar ta samar da wuraren kulawa da irin waɗannan yara yayin da iyayensu ke karɓar magani.
Cutar na ci gaba da yaɗuwa cikin sauri, inda aka samu sama da mutum 5,000 da suka harbu.