Home » ‘Yan Sanda 272 Sun Samu Karin Girma A Kano

‘Yan Sanda 272 Sun Samu Karin Girma A Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Mujahid Wada Musa

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta yi bikin kara wa jami’an ta 272 girma, a matakai daban-daban kamar yadda hukumar kula da aiyukan yan sanda ta kasa PSC ta amince.

An gudanar da bikin karin girman a wajen shakatawar manyan jami’an yan Sanda dake unguwar Bompai a ranar Litinin.

Kwamishinan yan sandan jihar Kano CP Salman Dogo Garba, ya taya wadanda suka samu karin girman, Inda yaja hankalin su kan ci gaba da jajircewa kan aikinsu.

Cikin wadanda likafar ta su ta daga sun hada da, mataimakan kwamishinan yan sanda 4, sai mutane 50 daga matakin SP zuwa CSP sai mutane 32 daga DSP matakin zuwa SP da kuma mutane 286 daga matakin ASP zuwa DSP.

Rundunar ta ce wannan rana ce ta farin ciki agare su, da wadanda suka samu karin girman da kuma iyalansu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?