Home » Yan Sanda Dubu 45,000 Ne Za Su Kula Da Zaben Jihar Anambra

Yan Sanda Dubu 45,000 Ne Za Su Kula Da Zaben Jihar Anambra

Babban Sifeton ƴansandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya amince da aika jami'an ƴansanda 45,000 domin bayar da tsaro a lokacin zaɓen gwamnan jihar Anambra da za a yi ranar 8 ga watan Nuwamban 2025.

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Babban Sifeton ƴansandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya amince da aika jami’an ƴansanda 45,000 domin bayar da tsaro a lokacin zaɓen gwamnan jihar Anambra da za a yi ranar 8 ga watan Nuwamban 2025.

Egbetokun – wanda kwamishinan ƴansanda mai lura da dakarun kai ɗaukin gaggawa – ya bayyana hakan ne ranar Talata a lokacin wata ganawa da kwamitin haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da aka gudanar a shalkwatar hukumar zaɓen ƙasar da ke Abuja.

Babban Sifeton ƴansandan ya ce jami’an da za a tura za su tabbatar da tsaro a kafin zaɓen da lokacin zaɓen da ma bayan zaɓen.

Ya ƙara da cewa za a fara tura jami’an ne tun daga ranar 1 ga watan Nuwamba domin kawar da duk wata barazana ga zaɓen.

Egbetokun ya kuma ce baya ga jami’an ƴansanda akwai sauran hukumomin tsaro da za su taka rawa a zaɓukan da suka haɗa da na farin kaya, DSS da rundunar tsaron fararen hula da sibil difens da sojoji.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?