Jami’an tsaron hadin gwiwa na Scorpion Squad, sun sami nasarar kama shararren mai garkuwa da mutanen nan ,Sha’aibu Alhaji Ahijo, wanda hukumar tsaron farin kaya ta DSS ke nemansa ruwa a jallo.
Ahijo mai shekaru 25, an kama shi ne karkashin gadar Nyanya dake birnin tarayya Abuja, a ranar 24 ga watan Maris 2025 da misalin karfe 6:00pm na yamma bisa samun bayan sirri da jami’an tsaron suka yi.
Da yake amsa tambayoyin jami’an tsaron, ya tabbatar da cewa an kashe yaransa uku da suka hada da Musa, Babangida da kuma wani da ba a bayyana sunansa ba, a wani yunkurin garkuwa da mutane a jihar Benue.
- Sarkin Kano Na 15 Ya Haƙura Da Hawan Sallah
- Mutane 2 Sun Rasu Wasu Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Kano
An kama shi ne a shirye-shiryen da yake yi na sake kafa gungun masu garkuwa da mutanen a birnin tarayya Abuja.
Yanzu haka dai hukumomin tsaron sun tabbatar da cewa wanda ake zargin yana basu hadin kai wajen gudanar da bincike.