Home » Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Daddatsa Mahaifinsa A Jigawa

Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Daddatsa Mahaifinsa A Jigawa

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Rundunar yan sandan jihar Jigawa ta bayyana  cewa yanzu haka tana tsare da wani matashi bisa zarginsa da daddatsa mahaifinsa da Adda, wandada hakan ya yi sanadiyar rasuwarsa.

Kakakin ruazndunar yan sandan jihar , SP Shiisu Lawan Adamu , ne ya tabbatar da hakan a wani takaitaccen sako da ya aike wa da MUHASA TVR.

Sanarwar ta ce matashin da ake zargi yana da shekaru 20, amma rundunar bata bayyana sunansa ba ko kuma garin da ya fito.

SP Shisu Lawan ya tabbatar da cewa sun fara gudanar da bincike akansa kuma za su yi wa al’umma Karin haske anan gaba kadan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?