Home » ‘Yan Sandan Najeriya Sun Fara Aiwatar Dokar Inshorar Motoci

‘Yan Sandan Najeriya Sun Fara Aiwatar Dokar Inshorar Motoci

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Mai magana da yawun ‘yan sandan Najeriya a Legas, Benjamin Hundeyin, ya ce wannan shirin na inganta insharar motoci zai tabbatar da cewa masu motoci masu bin tituna sun sami kariya.

‘yan sandan ya ce aiwatar da dokar, wanda aka fara a Legas a ranar Asabar, na bin umarnin Sufeto-Janar na ‘yansanda, Kayode Egbetokun, wanda ya bukaci a tabbatar da cewa duk masu ababen hawa sun mallaki inshorar motocin mai inganci.

Ya bukaci direbobi da masu ababen hawa su bi doka da oda, yana mai cewa wadanda suka saba za a hukunta su.

Mai magana da yawun ‘yan sanda ya kuma bukaci jami’an da ke aiwatar da dokar su nuna kwarewa a yayin gudanar da aikinsu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?