‘Yan Sandan Najeriya Sun Janye Gayyatar Sarki Muhammadu Sunusi II

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta janye gayyatar da ta yi wa Sarkin Kano na 16 Malam Muhammadu Sunusi II. 

Wannan na ƙushe a cikin wata sanarwar da Rundunar ta fitar da jami’in hulɗa da jama’a na ƙasa ACP Olumuyiwa Adejobi ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta ce rundunar ta janye gayyatar ne biyo bayan shawarar da masu ruwa da tsaki suka basu da kuma gudun kar a yi wa aikin rundunar mummunar fahimta ko kuma a mayar da batun siyasa.

Maimakon sarkin ya je Abuja domin amsa tambayoyin rundunar, Sufeton ‘yan sanda na na ƙasa Kayode Egbetokun ya umarci ‘yan sandan da ke sashen tattara bayanan sirri su je Kano domin jin ta bakin Sarkin dangane da abin da ya faru a lokacin bukukuwan ƙaramar sallah.

Bayyanar wannan sanarwa ta janyo mabanbanta martani daga ‘yan Najeriya a kafafen sada zumunta.

Post masu alaƙa

‘Talauci ya faɗo daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha