• Home  
  • Yar Shekaru 14 Ta Nutse A Kogi A Kokarin Diban Ruwa
- Babban Labari

Yar Shekaru 14 Ta Nutse A Kogi A Kokarin Diban Ruwa

  Daga: Safiyanu Haruna Kutama Wata yarinya ‘yar shekara 14 mai suna, Elizabeth Peter, daga unguwar Korokpa, a karamar hukumar Paikoro a jihar Neja ta nutse a kogin Chanchaga , a lokacin da ta ke kokarin diban ruwa. Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, inda Elizabeth ta je kogin tare da ’yan uwanta domin […]

 

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Wata yarinya ‘yar shekara 14 mai suna, Elizabeth Peter, daga unguwar Korokpa, a karamar hukumar Paikoro a jihar Neja ta nutse a kogin Chanchaga , a lokacin da ta ke kokarin diban ruwa.

Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, inda Elizabeth ta je kogin tare da ’yan uwanta domin diban ruwa, amma ta fada cikin rami mai zurfi a cikin kogin.

 

Elizabeth, dalibar SS1 ce a  Saint Andrew Academy, Tunga Minna, an ce tana daya daga cikin wadanda kogin ya rutsa da su.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ana samun mace-mace a duk shekara saboda  ramuka ma su zurfi da ke cikin kogin, wanda ke haifar da hatsarin ga mutane da yawa.

Kawarta, Abigail Idoko, ta ce ‘’ wannan lokacin shi ne karon farko da Elizebeth ta je kogin ranar Asabar bayan ta kasa samun masu sayar da ruwa da za su saya.

Ta kuma bayyana cewa an dauki kimanin sa’o’i biyu kafin a ceto Elizabeth daga  cikin ramukan da ke da zurfi.

 

A lokacin da majiyar mu ta ziyarci ‘yan uwan wadanda suka rasu a Korokpa, mahaifiyarta ta cika da mamaki, yayin da aka ce mahaifinta, Mista Peter, wani jami’in soji yana jihar Zamfara yana bakin aiki.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai