Home » Yar Shekaru 14 Ta Nutse A Kogi A Kokarin Diban Ruwa

Yar Shekaru 14 Ta Nutse A Kogi A Kokarin Diban Ruwa

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

 

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Wata yarinya ‘yar shekara 14 mai suna, Elizabeth Peter, daga unguwar Korokpa, a karamar hukumar Paikoro a jihar Neja ta nutse a kogin Chanchaga , a lokacin da ta ke kokarin diban ruwa.

Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, inda Elizabeth ta je kogin tare da ’yan uwanta domin diban ruwa, amma ta fada cikin rami mai zurfi a cikin kogin.

 

Elizabeth, dalibar SS1 ce a  Saint Andrew Academy, Tunga Minna, an ce tana daya daga cikin wadanda kogin ya rutsa da su.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ana samun mace-mace a duk shekara saboda  ramuka ma su zurfi da ke cikin kogin, wanda ke haifar da hatsarin ga mutane da yawa.

Kawarta, Abigail Idoko, ta ce ‘’ wannan lokacin shi ne karon farko da Elizebeth ta je kogin ranar Asabar bayan ta kasa samun masu sayar da ruwa da za su saya.

Ta kuma bayyana cewa an dauki kimanin sa’o’i biyu kafin a ceto Elizabeth daga  cikin ramukan da ke da zurfi.

 

A lokacin da majiyar mu ta ziyarci ‘yan uwan wadanda suka rasu a Korokpa, mahaifiyarta ta cika da mamaki, yayin da aka ce mahaifinta, Mista Peter, wani jami’in soji yana jihar Zamfara yana bakin aiki.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?