Zaɓe: Atiku da Obi sun Garzaya Kotun Koli

Alhaji Abubakar Atiku, ya bukaci kotun koli ta soke hukuncin da kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa (PEPC) ta yanke, wanda ya tabbatar da Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

A cikin kunshin daukaka karar da Atiku ya shigar a gaban kotun koli, ya gabatar da hujjarsa a kan wasu dalilai 35, inda ya dage cewa kotun zabe a hukuncin da shugabanta, Mai shari’a Haruna Simon Tsammani, ya yanke, ta aikata babban kuskure da rashin adalci a sakamakon binciken da ta kammala.

Shi ma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya yi makamancin zargin tare da ɗaukaka ƙara zuwa kotun daga ke sai Allah-ya-isa.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr