Home » Ɗalibar Jami’a Ta Mutu A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Karɓar Kuɗin Fansa Da Babura

Ɗalibar Jami’a Ta Mutu A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Karɓar Kuɗin Fansa Da Babura

Ɗalibar Jami’ar Tarayya ta Gusau Zarah Abubakar Shehu, ƴar shekaru 21 ta rasu a hannun masu garkuwa da mutane bayan ta kwashe watanni huɗu a tsare. 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Ɗalibar Jami’ar Tarayya ta Gusau Zarah Abubakar Shehu, ƴar shekaru 21 ta rasu a hannun masu garkuwa da mutane bayan ta kwashe watanni huɗu a tsare. 

Zarah, wacce dalibar aji na 3 ce, an sace ta daga gidansu da ke unguwar Damba a Gusau da sanyin safiyar Lahadi, 3 ga watan Nuwamba, shekarar 2024, lokacin da ‘yan bindiga suka farmaki yankin.

Da farko masu garkuwar sun bukaci a biya su naira miliyan 35, amma daga baya an cimma matsaya kan naira miliyan 10.

Duk da haka, bayan an biya kudin fansa, masu garkuwa sun ki sakin Zarah. Sun bukaci a kawo musu babura hudu (Boza) da katon hudu na man inji kafin su sake ta

Bayan watanni ana kokarin cika wadannan bukatu, an samu damar samar da kayayyakin da suke so.

Amma da aka sanar da shugaban masu garkuwa, sai ya kira mutanensa, inda suka bayyana cewa Zarah ta mutu kuma an binne.

Zarah ita ce ‘ya mace guda tilo ga mahaifiyarta, kuma ta shafe watanni huɗu a hannun masu garkuwa da ita.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?