Home » Ɗan Bindiga Ya Kuɓutar Da Gwarzon Gasar Karatun Alkur’anin Da Aka Sace A Katsina 

Ɗan Bindiga Ya Kuɓutar Da Gwarzon Gasar Karatun Alkur’anin Da Aka Sace A Katsina 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Iyayen gwarzon gasar karatun Alkur’anin da aka sace a Katsina Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa a Jihar Katsina, sun bayyana cewa sun kuɓuta daga hannun ’yan bindiga ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

An sace Abdulsalam, wanda ya lashe gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa da aka gudanar a Jihar Kebbi tare da mahaifinsa ne makonni biyu da suka gabata, bayan Gwamnan Katsina Mal Umaru Dikko Radda ya karrama shi.

Mahaifinsa, Malam Rabiu Zakariya Faskari, ya shaidawa manema labarai cewa suna tsare a hannun ’yan bindiga a Katsina har sai da wani babban ɗan bindiga mai suna Yellow daga Zamfara ya zo ya karɓe su da ƙarfi.

“Ya yi wa masu garkuwa duka kafin ya tafi da mu,” in ji shi.

Ya ce an yi ciniki kan fansa amma Yellow ya ƙi yarda.

“Muna ta addu’a har ranar Juma’a da aka zo aka ce mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauke mu suka kai mu wani gari, daga nan muka yi tafiyar awa huɗu kafin muka samu mota.”

Malam Rabiu, ya ce da suka hau babur sai direban ya shaida musu cewa an kashe Yellow.

“Ashe mutuwarsa ce ta sa yaransa suka sake mu muka koma gida.”

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?