Home » Ɗangote Ya Ziyarci M.Babandede OFR, OCM

Ɗangote Ya Ziyarci M.Babandede OFR, OCM

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaban rukunin kamfanonin Ɗangote Alhaji Aliko Dangote ya kai ziyarar ta’aziyya gidan tsohon shugaban hukumar shigi da fici ta Najeriya kuma mamallakik tashar MUHASA Muhammad Babandede OFR, OCM bisa rasuwar Mahaifiyarsa Hajiya Hajara Muhammad.

Ɗangote ya ziyarci Babandede ne a gidansa da ke brinin Kano kwanaki shida bayan rasuwar. 

Yayin ziyarar ta’aziyyar, Ɗangote ya yi addu’ar Allah ya gafartawa Hajiya Hajara, ya ce rashin ta ba iya iyalanta ya shafa ba, lura da cewa ta raini mutane da yawa. 

Alhaji Aliko Dangote ya kuma hori iyalanta da suyi koyi da managartar halayenta.

Ya yi adduar Allah ya basu hakuri domin jure wannan babban rashi da akayi.

Da yake karbar gaisuwar, Muhammad Babandede ya godewa Alhaji Aliko Dangote da wannan taaziya, tare da yi Masa addu’ar Allah ya maida shi gida lafiya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?