Kwara: Wani Alƙalin Alƙalai Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Allah ya yi wa Tsohon alƙalin alƙalan kotun ɗaukaka ƙara ta shari’ar musulunci ta jihar Kwara rasuwa, mai shari’a Abdulmutallib Ahmad Ambali.

Marigayin ya rasu ne a safiyar yau Alhamis a asibitin koyarwa na jami’ar Ilorin (UITH), Oke-Oyi, bayan ƴar gajeruwar rashin lafiya.  Ya rasu yana da shekara 83 a duniya. 

Marigayin shine alƙalin alƙalai na biyu bayan mai shari’a Abdulkadir Orire, kuma rajistara na farko a kotun ɗaukaka ƙara ta shari’ar musulunci a jihar Kwara.

Marigayi Abdulmutallib Ahmad Ambali ya kwashe shekara 8 a kujerar alƙalin alƙalan daga shekarar 2001 zuwa 2008.

A wata tattauna ta manema labarai, alƙalin alƙalan musulunci na jihar Kwara, mai shari’a Abdullateef Kamaldeen wanda ya tabbatar da rasuwar, ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai tsoron Allah, haziƙin alƙali wanda yayi riƙo da koyarwar addinin musulunci.

Ya bayyana marigayin a matsayin mutumin kirkiri, mai riƙo da addini, mai kyawawan halaye wanda baya raina kowa.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr