Kano: Ƙungiyar ‘Yan Jaridu, NUJ, Ta Taya Abba Kabir Yusuf Murna Lashe Zaɓe

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa, reshen jihar Kano, ta taya zaɓaɓɓen Gwamnan jihar na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf murnar samun nasara a zaɓen Gwamnan da aka gudanar.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Shugaban ƙungiyar Kwamared Abbas Ibrahim, ta tabbatar da cewa Abban zai kai jihar matakin ci gaba ta fuskar ayyukan raya ƙasa da ci gaban al’umma, duba da ƙwarewar da yake da ita da kuma kasancewarsa Injiniya.

Daga ƙarshe kuma ƙungiyar ‘yan jaridun ta yi addu’ar Allah ya yi riƙo da hannun zaɓaɓɓen Gwamnan, kuma ta yi fatan harkar yaɗa labarai  ta sami tagomashi a sabuwar gwamnatin.

Post masu alaƙa

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China

Babandede Ya Taya Shettima Murnar Sake Samun Takarar Mataimakin Shugaban Kasa