• Home  
  • An Ba Gwamnatin Najeriya Wa’adin Ceto Ɗalibai 20
- Babban Labari - Labarai

An Ba Gwamnatin Najeriya Wa’adin Ceto Ɗalibai 20

Shugaban ƙungiyar ɗaliban Najeriya, Muhammad Sabo ya shaida wa manema labarai cewa a wannan karon ƙungiyar baza ta zuba ido taga ana cutar da ɗaliban ba.

Daga Mubarak Ibrahim Mandawari

Ƙungiyar ɗaliban Najeriya ta ƙasa {NANS} ta ba gwamnatin tarayya wa’adin mako biyu da ta ceto wasu ɗaliban koyan aikin likita su ashirin, da ƴan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Binuwai.

Shugaban ƙungiyar ɗaliban Najeriya, Muhammad Sabo ya shaida wa manema labarai cewa a wannan karon ƙungiyar baza ta zuba ido taga ana cutar da ɗaliban ba.

Ya ƙara da cewa gaza ceto ɗaliban zai sa a ga fushin su fiye da yadda aka saba gani.

Wannan dai ba shine karon farko da ake sace ko kuma garkuwa da ɗaliban ƙasar ba, a hanyar su ta komawa gida ko kuma a cikin ɗakunan kwanansu dake cikin makarantu.

Jihar Zamfara sun fuskanci irin wannan matsalolin a baya.

Ɗalibai masu shirin bautar ƙasa suma basu tsira daga ayyukan ƴan bindigan ba,a baya an yi dasu a kan hanyoyin su na shiga dandalin horas da ƴan hidimtawa ƙasa, musamman a hanyoyin sakkwato, Zamfara da Kebbi.

Ɗaliban ƙasar sun fuskanci matsaloli da suka haɗa da yajin aiki kashi-kashi, harda wanda aka shafe watanni shida wanda hakan ya tsayar da karatunsu baki ɗaya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000