A gaggauta sakin ’yan Najeriya 42 da aka kama a Mozambique — NiDCOM

Hukumar ’Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM) ta buƙaci mahukuntan ƙasar Mozambique su gaggauta sakin ’yan Najeriya 42 da aka kama a ƙasar ba tare da bayyana takamaiman laifin da suka aikata ba.

Shugabar hukumar, Abike Dabiri-Erewa, ta bayyana damuwa kan lamarin, tana mai cewa kama ’yan Najeriya ba tare da tuhuma ba abin takaici ne kuma ya kamata a sake su ko kuma a gurfanar da su a gaban kotu idan sun aikata wani laifi.

A wata sanarwa da kakakin NiDCOM, Abdur-Rahman Balogun, ya fitar a Abuja ranar Lahadi, Dabiri-Erewa ta ce abin damuwa ne yadda aka kama ’yan Najeriya kaɗai a yayin wani samame da aka kai a wata kasuwar sayar da kayan gyaran motoci.

Ta ce rahotanni sun nuna cewa an bar ’yan kasuwa na wasu ƙasashe da ke wurin, yayin da aka kama ’yan Najeriya kaɗai, lamarin da ta ce na iya nuna wariya ko nuna ƙyama ga ’yan ƙasar.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya