A yau Talata Ake Jiran Isowar Shugaban Kasar Najeriya, Tinubu, daga kasar waje

A yau Talata ake sa ran dawowar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu Najeriya

Wata majiya a fadar shugaban kasa ta bayyana cewa shugaba Tinubu wanda ya bar kasar a ranar 20 ga watan Yuni zuwa birnin Paris na da niyyar komawa Najeriya don yin bukin babbar Sallah a gida.

An shirya cewa Shugaban kasar, zai koma Abuja daga Paris a ranar Asabar da ta gabata, amma daga nan sai ya wuce birnin Landan don gudanar da ziyara ta kashin kansa.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr