Home » Alh. Muhammad Babandede Ya Zama Jagora A Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai Ta Ƙasa

Alh. Muhammad Babandede Ya Zama Jagora A Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai Ta Ƙasa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai Ta Najeriya IBAN ta naɗa Alhaji Muhammad Babandede OFR muƙamin jagora a tafiyar ƙungiyar ta ƙasa domin neman cigaba da bunƙasa harkokinta. 

Alhaji Muhammad Babandede OFR, OCM wanda ya riƙe shugabancin Hukumar Shigi da Fici ta Ƙasa (Immigration) shine mamallakin tashoshin radiyo da talabijin na MUHASA da ke yaɗa shirye-shirye a mita 92.3fm Kano da ta intanet a www.muhasatvr.ng.

Yayinda MUHASA TV ke yaɗa shirye-shirye a tasha ta 170 a dikodar StarTimes.

Alhaji Babandede wanda gogaggen ma’aikaci ne ya samu muƙamin ex-officio a IBAN domin kawo cigaba a harkokin kafafen yaɗa labarai a Najeriya.

Sabon jagoran a IBAN ya sha alwashin bada gudummawarsa musamman wurin yaƙi da labaran ƙarya da ke samun wurin zama a harkokin aikin jarida a Najeriya.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?