Allah Ya Yi Wa Rajistaran Jami’ar Bayero Rasuwa

Wannan sanarwa wannan rashi da jami’ar Bayero ta yi, ya fito ne daga hannun Daraktan Hulɗa da Jama’a na Jami’ar Bayero Kano, Malam Lamara Garba.

Ya bayyana cewa Rajistaran ya rasu da sanyin safiya ranar Laraban nan.

Inda aka gudanar da sallar jana’iza da ƙarfe goma 10:00 na safe a babban masallacin dake sabon reshen jam’iyyar ta Bayero.

Malam Jamilu Ahmed Salim, ya shafe tsawon shekaru huɗu a matsayin rajistaran Jami’ar kuma Malam Lamara ya bayyana shi a matsayin haziƙi wanda ya ba da gudunmuwa mai yawan gaske ga cigaban jami’ar.

Sannan ya yi addu’ar Allah ya gafarta masa tare da saka masa da gidan Aljanna.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro