Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Kwashe Ma’aikatanta Daga Sudan

Majalisar Ɗinkin Duniya ta kwashe ɗaruruwan ma’aikatanta da iyalansu daga Khartoum da sauran yankunan Sudan, a cewar wani mai magana da yawun Babban Sakataren ƙungiyar.

Antonio Guterres ya yi ta nanata kiraye-kirayen a tsagaita wuta domin barin fararen hula su fice daga yankunan da rikice-rikicen ya shafa.

Mai magana da yawun Babban Sakataren ya ƙara da cewa Majalisar Ɗinkin Duniya za ta ci gaba da aiki da ma’aikatanta da ke ciki da wajen Sudan saboda har yanzu shugaban harkokin diflomasiyyarta, Volker Perthes, yana cikin ƙasar.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.

Rundunar yan sandan Kano ta kwato motar da aka sace sannan aka siyar da ita a Nijar