Amotekun ta ceto ma’aikatan lafiya 3 da wasu 2 da aka sace

Rundunar Tsaro ta Jihar Ondo, Amotekun Corps, ta ceto mutane biyar a cikin ayyuka biyu da aka yi a dare guda a karamar hukumar Akure ta Kudu.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya rawaito cewa, a misalin ƙarfe 2 na safe a ranar Asabar, ma’aikatan da ke aikin dare a cibiyar lafiya da ke Oke-Ijebu, cikin birnin Akure, an sace su.

Rahotanni sun bayyana cewa masu garkuwa sun isa wurin a cikin babbar bas, sun karbe cibiyar lafiya da karfi da ke gaban babbar makaranta, sannan suka dauki ma’aikatan lafiya.

Mista Adetunji Adeleye, Kwamandan Amotekun, wanda ya tabbatar da haka a ranar Asabar a Akure, ya ce an ceto ma’aikatan lafiya guda uku da wasu mutane biyu.

“Wani mutum mai shekaru 45 da ɗansa mai shekaru 15 an sace su a Pelebe da ke bakin hanyar Oda Akure tsakanin ƙarfe 7:30 da 8:00 na yamma, amma dakarun kare ta kwana na Amotekun sun ceto su da misalin ƙarfe 1 na safe bayan yin wani yaki mai tsanani da masu garkuwa.

“Haka kuma, ma’aikatan lafiya guda uku da aka sace tun farko sun samu ‘yanci a misalin ƙarfe 4:30 na safe kuma yanzu suna karbar magani a cibiyar lafiya ta Amotekun,” in ji shi.

Adeleye ya tabbatar wa mazauna jihar cewa kiyaye rayuka da dukiyoyi na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ke fifita.

Kwamandan ya kuma yi kira ga jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai cikin lokaci ga hukumomin tsaro, inda ya jaddada bukatar hadin kai don inganta tsaro a fadin jihar.

Post masu alaƙa

Yan bindiga sun sace shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

A riƙa yi wa masu shirin aure gwajin miyagun ƙwayoyi :- Buba Marwa