Sojin Najeriya sun kashe ‘yan ta’addar ISWAP 38 a jihar Borno.

Kakakin rundunar da take yaki da yan ta’adda a arewa maso gabashin najeriya Llaftanar Kanal Sani Uba ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa daya fitar a yau asabar.

Sanarwar tace yan ta’addar sun kai wani sansanin sojojin hari a yakin mandaragirau dake jihar Borno to amman sojojin suka bude musu wuta.

Kamar yadda ya bayyana sojojin tsanan ta wuta kan yan ta’addar wanda yasa suka sami kashe guda 38.

Sanarwar tace daga nan kuma sojojin sama suka kawo dauki inda suka bude musu wuta ta sama.

Ta kuma bayyana cewa sauran yan ta’addar sun zubar da makaman su inda tsere zuwa daji.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda