Ma’aikatar Kasuwanci ta Jamhuriyar Nijar ta haramta fitar da gero da shinkafa daga kasar
A sanarwar, ministan kasuwancin na kasar Alkache Alhada ya bukaci jami’an ma’aikatarsa da na hukumar hana fasa-kwauri da jami’an tsaro da su kama sannan su hukunta duk wanda suka kama da laifin fitar da wadannan kayayyaki.