Hisba ta kama mutane 7 dake musayar matansu na aure

Hukumar Hisba a shiyyar Katagum ta jihar Bauchi ta yi nasarar kama wasu mutane bakwai da ake zargi da aikata wani sabon salo na musayar mata domin hulɗar aure da jima’i a tsakanin su, a Azare cikin ƙaramar hukumar Katagum. Bayanan hakan ya fito ne daga bakin Kwamandan Hisba na shiyyar Katagum, Malam Ridwan Muhammad […]

Read more

Danjuma Goje ya yi fatali da maslaha a Gombe ta Tsakiya

Sanatan da ke wakiltar Gombe ta Tsakiya, Muhammad Danjuma Goje, ya yi fatali da tsarin maslaha da Jam’iyyar APC ta Jihar Gombe ta bi wajen tsayar da ’yan takara, yana mai cewa matakin ya saɓa da dokokin zaɓe da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyya. Wannan na zuwa ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar […]

Read more

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu a matsayin rancen sayen ababen hawa ga ma’aikatan jiha da na kananan hukumomi cikin shekaru uku da suka gabata. Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan yayin jawabi a bikin ranar ma’aikata ta bana, kamar yadda Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito. Ya ce […]

Read more