DSS ta kama wanda ya sace yaro dan shekara 5 a Kano

Hukumar  tsaron ta farin kaya (DSS) ta samu nasarar ceto wani yaro mai shekaru biyar, mai suna Muhammad Haruna, daga hannun masu garkuwa da mutane a Kauyen Danzaki, karamar hukumar Gezawa. An gudanar da aikin ceton ne da misalin ƙarfe 7:40 na yamma ranar Alhamis, bayan an sami rahoton cewa an sace yaron kuma masu […]

Read more

Yadda Aka Karrama Janar Murtala Muhammed A Abuja

Manyan mutane sun hallara a Abuja, a ranar Juma’a, domin tunawa da cika shekaru 50 da kisan tsohon Shugaban ƙasa, Janar Murtala Muhammed. An kashe marigayi Janar ne tare da wasu muƙarrabansa, a wani yunƙurin juyin mulki da bai yi nasara ba a Legas, ranar 13 ga Fabrairu, 1976. Jami’an rundunar sojin Najeriya sun yi […]

Read more

Ana Fargabar Ɓullar Zazzaɓin Lassa A Gombe

An samu rahoton wasu mutane huɗu da ake zargin sun kamu da cutar zazzaɓin Lassa a Jihar Gombe, sa’o’i kaɗan kafin ƙaddamar da shirin ‘Ranar Ba Da Gudunmawar Jini’  wanda aka shirya gudanarwa a ranar Asabar. Majiyoyi daga Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Gombe sun bayyana cewa, daga cikin mutanen huɗun da ake zargin har da […]

Read more

Kotu ta yanke wa Samha hukuncin ɗaurin wata shida

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ta yanke wa jarumar fina-finan Kannywood Samha M Inuwa hukuncin ɗaurin wata shida saboda samunta da laifin wulakanta naira. Makonni biyu da suka gabata ne jami’an hukumar EFCC, mai yaƙi da almundahanar kuɗi a Najeriya ta suka kama jarumar bayan ɓullar wani bidiyo da a ciki take face […]

Read more

INEC ta saka ranar zaɓen 2027

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya Inec ta fitar da jadawalin manyan zaɓuɓɓukan kasar na shekarar 2027, inda ta bayyana muhimman ranakun zaɓe da na zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa da yakin neman zaɓe, da rajistar masu zaɓe. Hukumar ta ce za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya ranar […]

Read more

EFCC sun gayyace ni – El-Rufai

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa hukumar EFCC ta aika masa da takardar gayyata zuwa ofishinta, kuma ya amince zai je. Ya bayyana haka ne a wata hira da BBC inda ya ce “Efcc sun rubuto min takadar gayyata zuwa ofishinsu, kuma na amsa musu zan je ranar Litinin mai zuwa” Wannan […]

Read more