Wata Kotun Majistare da ke Jos a ranar Juma’a ta yanke wa wani ɗan kasuwa mai suna Shederack Danlami mai shekaru 22 hukuncin daurin watanni hudu a gidan yari bisa samunsa da laifin satar zakaru biyu.
Mai shari’a Shawomi Bokkos ta gurfanar da wanda ake tuhuma tare da yanke masa hukunci bayan ya amsa laifinsa.
Mai Shari’a Bokkos, a hukuncin da ta yanke, ta baiwa mai laifin zabin biyan tarar N20,000.
Tun da farko, ɗan sanda mai shigar da kara, sufeto Daniel Longwal, ya shaida wa kotun cewa, an kai karar ɗan kasuwar ofishin ‘yan sanda na Anglo-Jos a ranar 25 ga watan Maris, da wata tawagar ‘yan banga.
Longwal ya ce wanda aka yankewa hukuncin ya saci zakaru biyu kuma ya yankasu wanda farashin su ya kai Naira 20,000.
- Wajen Da Basiru Dankiri Yake Tsare Shekaru 10 A Kano.
- Cikin Hotuna: Yan Sandan Kano Sun Kama Masu Aikata Laifuka 78 Cikin Kwana 16.
Mai gabatar da kara ya ce laifin ya saba wa tanadin sashe na 286 na dokar Penal Code na jihar Filato. (NAN)