An Ga Watan Ƙaramar Sallah a Najeriya 

Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Alhaji Abubakar Sa’ad III ya bayyana cewa an ga watan Shawwal a Najeriya dan haka za a idin ƙamar salla ranar Lahadi. 

Tun da yammacin ranar Asabar ne dai aka bayyana ganin watan Shawwal a ƙasar Saudiyya, kafin daga bisani a samu labarin ganin shi a jamhuriyar Nijar.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana ganin watan ne a fadar sa da ke Sakkwato, Arewa maso yammacin tarayyar Najeriya kamar yadda ya saba.

Kawo yanzu dai ‘yan Najeriya na cigaba da bayyana murnar kammala ibadar watan Ramadan, suna kuma fatan Allah ya karɓa.

Post masu alaƙa

An dakatar da shugaban NSCDC a Neja kan mutuwar masu haƙar ma’adanai 37

Rundunar yan sandan jihar Kano, ta raba wa iyalan jami’anta 62 sama da Naira miliyan 34

Gwamnati ta sa dokar hana fita bayan ɓarkewar zanga-zanga a Neja