An ga watan Ramadan a Najeriya

Hukumomin ƙasar sun sanar da ganin jinjirin watan azumin watan Ramadan na bana, wanda hakan ke nufin za a fara azumin daga gobe Laraba 17 ga watan Fabrairu a ƙasar ta Saudiyya.

Shafin Haramain ne ya sanar da haka a kafar X, inda shafin ya ruwaito cewa, “an ga jinjirin wata a ƙasar Saudiyya. Don haka za a fara azumin wata Ramadan na shekarar 1447 daga gobe,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Tuni dai hukumomi a Najeriya suka buƙaci musulman ƙasar su nemi jinjirin watan a yau Talata 17 ga Fabrairu 2026, wadda ta yi daidai da 29 ga watan Sha’aban 1447AH.

Buƙatar na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ta fito daga fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar.

Sanarwar ta buƙaci Musulmi su fara neman jinjirin watan azumi a wannan rana, tare da umartar duk wanda ya ga watan da ya kai rahoto ga shugaban ƙaramar hukuma ko Dagaci mafi kusa domin a isar da saƙon ga fadar Sarkin Musulmi.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda