An ga watan Ramadan a Najeriya

Hukumomin ƙasar sun sanar da ganin jinjirin watan azumin watan Ramadan na bana, wanda hakan ke nufin za a fara azumin daga gobe Laraba 17 ga watan Fabrairu a ƙasar ta Saudiyya.

Shafin Haramain ne ya sanar da haka a kafar X, inda shafin ya ruwaito cewa, “an ga jinjirin wata a ƙasar Saudiyya. Don haka za a fara azumin wata Ramadan na shekarar 1447 daga gobe,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Tuni dai hukumomi a Najeriya suka buƙaci musulman ƙasar su nemi jinjirin watan a yau Talata 17 ga Fabrairu 2026, wadda ta yi daidai da 29 ga watan Sha’aban 1447AH.

Buƙatar na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ta fito daga fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar.

Sanarwar ta buƙaci Musulmi su fara neman jinjirin watan azumi a wannan rana, tare da umartar duk wanda ya ga watan da ya kai rahoto ga shugaban ƙaramar hukuma ko Dagaci mafi kusa domin a isar da saƙon ga fadar Sarkin Musulmi.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya