An Kama Masu Kaiwa Yan Bindiga Man Fetur A Nijar

Wani samame da rundunar tsaron Nijar ta Garde Nationale ta gudanar ya bata damar kama wasu mutane shida da ake zargi da safarar man fetur ga kungiyoyi masu ɗauke da makamai.

An kama mutane shida da ake zargi ne a wani ɓangare na ayyukan da rundunar ta ƙaddamar cikin ƴan kwanakin nan domin yaki da ta’addanci da safarar man fetur da ake yi wa ƙungiyoyi masu tayar da ƙayar baya.

Jamhuriyar Nijar dai na fuskantar barazanar tsaro daga mayaƙa masu riƙe da bindiga, a daidai lokacin da ƙasar ke ci gaba da kasancewa a ƙarƙashin mulkin soji.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya