An Kama Masu Kaiwa Yan Bindiga Man Fetur A Nijar

Wani samame da rundunar tsaron Nijar ta Garde Nationale ta gudanar ya bata damar kama wasu mutane shida da ake zargi da safarar man fetur ga kungiyoyi masu ɗauke da makamai.

An kama mutane shida da ake zargi ne a wani ɓangare na ayyukan da rundunar ta ƙaddamar cikin ƴan kwanakin nan domin yaki da ta’addanci da safarar man fetur da ake yi wa ƙungiyoyi masu tayar da ƙayar baya.

Jamhuriyar Nijar dai na fuskantar barazanar tsaro daga mayaƙa masu riƙe da bindiga, a daidai lokacin da ƙasar ke ci gaba da kasancewa a ƙarƙashin mulkin soji.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda