An Kama Yan Nijeriya 106 Da Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi A India

Hukumomi a Indiya sun tuhumi ‘yan Najeriya 106 da laifin safarar miyagun ƙwayoyi a shekarar 2024 da ta gabata, kamar yadda jaridar Indian Express ta ruwaito.

Rahoton ya ce ‘yan Najeriyar na cikin jimillar mutum 660 ne da rahoton shekara na hukumar yaƙi da miyagun ƙwayoyi ya bayyana tare wasu daga ƙasashen Nepal (203), da Myanmar (25), waɗanda su ne suka fi yawa a jerin.

Kazalika, akwai ‘yan Bangladesh (18), da Ivory Coast (14), da Ghana (13), da Iceland (10) waɗanda aka tuhuma da laifukan ta’ammali da ƙwayoyi.

“Indiya na fama sosai wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi saboda faɗin ƙasa da take da shi,” a cewar Ministan Harkokin Cikin Gida Amit Shah.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda