An Naɗa Mace Ta farko Mai Magana Da Yawun Rundunar Sojin Nijeriya

An naɗa mace ta farko a matsayin mai magana da yawun rundunar sojin ƙasa ta Nijeriya.

Appolonia Anaele mai muƙamin Laftanar Kanar ce za ta karɓi muƙamin daga hannun Manjo-Janar Onyema Nwachukwu.

Bayanai sun ce muƙamin nata zai fara ne a ranar Talata 22, ga watan Afrilun da muke ciki.

Shekaru sama da 50 ke nan da kafa rundunar sojin ƙasa ta Nijeriya, kuma babu wata mace da ta taɓa riƙe wannan muƙami.

Duk da cewa kawo yanzu tana a matsayin mai riƙon muƙami ne, amma duk da haka wannan shi ne karon farko.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya