• Home  
  • An Ƙaddamar Da Jiragen Yaƙi Mara Matuƙa Da Aka Kera A Najeriya 
- Babban Labari - Labarai

An Ƙaddamar Da Jiragen Yaƙi Mara Matuƙa Da Aka Kera A Najeriya 

Rundunar sojin Nijeriya ta yi bikin ƙaddamar jiragen yaƙi marasa matuƙa da aka ce an ƙera a kasar a karon farko kuma mafi girma a nahiyar Afirka baki ɗaya.

Janar Christopher Musa ya bayyana jiragen a matsayin waɗanda za su kawo sauyi wajen tunkarar barazanar matsalolin tsaro a Najeriya.

Ya jaddada muhimmacin samar da hanyoyin tsaro na soji a cikin gida, da kuma ƙalubale a siyasar duniya wajen samar da kayyakin tsaro.

‘‘Jiragen za su taka muhimmiyar rawa wajen haɓaka ayyukan sojojinmu, musamman a duniyar da samar da kayyakin aikin soja na zamani ke cike da ƙalubale saboda siyasar duniya.’’

“Idan ba ku samar da abin da kuke buƙata ba, za ku kasance a ƙarƙashin wasu, ko da kuna da albarkatun kuɗi don samun su,” in ji shi.

Janar C Musa ya ƙara da cewa jiragen za su taimaka wa Najeriya wajen daukar matakan gaggawa don fuskantar kalubalen tsaro, tare da rage dogaro da kayayyakin ƙasashen ƙetare.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000