Ana cigaba da hako mutanen da gini ya danne a Sudan

Ana ci gaba da luguden wuta a biranen Khartoum da ma yankin yammacin Dafur a cewar shaidun gani da ido, duk da yunkurin kawo karshen rikicin da kasashen duniya ke yi.

Wani mummunan hari da aka kai ta sama a garin Ombada mai yar tazara da birnin Khartoum ya yi sanadiyar rayukan mutane 5 yayin da wasu 17 suka jikkata.

Masu aikin ceto na ci gaba da neman mutanen da suka makale a ɓaraguzan gine-gine lamarin da ya sa ake ganin adadin wadanda suka mutu ka iya karuwa.

Ya zuwa yanzu, sama da mutum dubu uku ne rikicin Sudan ya sa suka rasa rayukansu, a cewar wata kungiya mai tattara bayanan yaki.

Post masu alaƙa

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Venezuela ta sanar da ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.