GOMBE

Ana Fargabar Ɓullar Zazzaɓin Lassa A Gombe

An samu rahoton wasu mutane huɗu da ake zargin sun kamu da cutar zazzaɓin Lassa a Jihar Gombe, sa’o’i kaɗan kafin ƙaddamar da shirin ‘Ranar Ba Da Gudunmawar Jini’  wanda aka shirya gudanarwa a ranar Asabar. Majiyoyi daga Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Gombe sun bayyana cewa, daga cikin mutanen huɗun da ake zargin har da […]

Read more

An haramta sana’ar bola-jari a Gombe

Gwamnatin Gombe ta haramta sana’ar bola jari a duk faɗin jihar, bisa abin da ya kira barazanar tsaro da kuma zargin sana’ar da ƙarfafa ayyukan laifi. An yanke wannan shawara ne a wani taron Majalisar Tsaro na musamman da gwamnatin jihar ta gudanar tare da manyan jami’an tsaro, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, domin […]

Read more

Umar Chuso ya zama sabon kwamishinan ’yan sandan Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta sanar da naɗin CP Umar Ahmed Chuso a matsayin sabon Kwamishinan ’Yan Sandan jihar. Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce Babban Sufeton ’Yan Sanda (IGP) ne, ya tura CP Chuso zuwa Gombe. Tuni ya fara aiki a matsayin Kwamishinan ’Yan Sanda na 24 a jihar. Sanarwar ta ce […]

Read more

2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe

Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanninta a Jihar Gombe, inda ta jaddada muhimmancin haɗin kai da farfado da jam’iyyar tun daga matakin ƙananan hukumomi zuwa jiha gabanin zaɓen 2027. Taron ya halarta bayan zuwan wakilai daga dukkanin ƙananan hukumomin jihar. Mambobin jam’iyyar sun yaba da yadda komai ya gudana cikin lumana da tsari, abin […]

Read more

Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar maharba, sun samu nasarar tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da aikata laifuka a Jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da Adamawa. Rundunar ta samu nasarar ne bayan kama Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40 daga ƙauyen Tilde a Funakaye, a […]

Read more