Home » Atiku Ya Bayyana Matsayarsa Kan Cigaba Da Zama A PDP

Atiku Ya Bayyana Matsayarsa Kan Cigaba Da Zama A PDP

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Daga : Shareep Khaleepha

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa ya bar jam’iyyar PDP.

Dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023 ya sake jaddada goyon bayansa ga hadakar jam’iyyun siyasa don kayar da jam’iyyar APC a 2027.

Daily Trust ta rawaito cewa, a baya-bayan nan, rahotanni daban-daban sun nuna cewa Atiku yana tunanin barin PDP don shirin takarar shugaban kasa a 2027.

Rahotannin sun ce yana shirin komawa jam’iyyar SDP.

Amma a cikin wata sanarwa da ofishin yada labaransa ya fitar a ranar Asabar, an bayyana cewa tsohon mataimakin shugaban kasar na nan a matsayin cikakken mamba na PDP.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?