Rundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Edo, ta kama wani matashi mai suna Aireebiuwa dan shekaru 27 bisa samunsa da laifin yanke kan mutum sannan ya sanya a cikin wata Jaka.
Kakakin rundunar yan sandan jihar Edo, Moses Yamu, ya ce jami’ansu dake aiki a Evbuotubu tare da hadin gwiwar yan Banga ne suka samu nasarar kama wanda ake zargin.
Rahotanni na cewa an kama shi a ranar 7 ga watan Maris 2025 akan titin Igbinudu, karamar hukumar Oredo ta jihar.
Moses Yamu , ya kara da cewa lokacin da ake yiwa wanda ake zargin tambayoyi ya kasa bayar da gamshasshen bayani, lokacin da ake bincike akansa har ya tabbatar da cewa kan wani mutum ne da ya sare masa kai sannan ya jefar da gawarsa a kusa da, Ewaka Shopping Plaza.
wani dan uwan marigayin ya bayyana wa yan sanda cewa, gawar dan uwan sa ce mai suna Edobor Lawrence, mai shekaru 43.
Kwamishinan yan sandan jihar BettRundunar yan sanda ta kasa reshen jihar Edo, ta kama wani matashi mai suna Aireebiuwa dan shekaru 27 bisa samunsa da laifin yanke kan mutum sannan ya sanya a cikin wata Jaka.
Kakakin rundunarey Otimenyin ya jajantawa iyalan marigayin tare da bada tabbacin cewa rundunar ba zata bar wannan abu da wasa ba , domin da zarar ta kammala bincike zata gurfanar da shi a gaban kotu.
A karshe kwamishinan yan sandan ya shawarci matashi , su daina neman sai sun yi kudi ta kowacce hanya, domin hakan wata hanya ce da wasu ke fakewa da ita don aikata laifuka.