An Kama Mutum 1 Saboda Kashe Dogarin Sarki Sanusi Na 2
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya reshen jihar Kano ta ce ta kama wani da take zargi da kashe wani jami’in tsaron Sarkin Kano Na 16 Malam Muhammadu Sanusi yayin aikin sa-kai a filin Idi.
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya reshen jihar Kano ta ce ta kama wani da take zargi da kashe wani jami’in tsaron Sarkin Kano Na 16 Malam Muhammadu Sanusi yayin aikin sa-kai a filin Idi.
Iyayen gwarzon gasar karatun Alkur’anin da aka sace a Katsina Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa a Jihar Katsina, sun bayyana cewa sun kuɓuta daga hannun ’yan bindiga ba tare da biyan kuɗin fansa ba.
Sabon tsarin sayar da man fetur a Najeriya ya haifar da ƙarin farashi, inda ake sayar da kowace lita a kan Naira 930 a Legas da kuma Naira 960 a Arewacin ƙasar.
Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Alhaji Abubakar Sa’ad III ya bayyana cewa an ga watan Shawwal a Najeriya dan haka za a idin ƙamar salla ranar Lahadi.
Rundunar ’yan Sandan Najeriya sun ce sun kama mutane 14 da ake zargi da hannu a kisan matafiya 16 ’yan Arewa a kan titin Uromi zuwa Obajana, a Jihar Edo.
Rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Ɗan Mudale da ya addabi mazauna yankin Tsafe da yankunan dake makwabtaka.
Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan mutane 16 da aka yi a jihar Edo, yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.
Jagoran jam’iyyar adawa ta NNPP kuma tsohon Gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso,da tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma ɗantakarar shugabcin ƙasar a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar sun yi tir da kisan ‘yan Arewa a jihar Edo, inda suka nemi a gudanar da bincike.
Ƙungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International ta ce mutane 16 aka kashe a mummunan kisan gillar jihar Edo ’yan asalin Kano ne, Arewa maso Yammacin Najeriya.
Sakataren Labarai na Fadar Gwamnatin Edo, Fred Itua ya ta tabbatar da cewa ’yan sa- kai ne suka kai mummunan hari kan waɗansu matafiya ‘yan Arewacin Najeriya, amma binciken farko ya tabbatar da cewa ‘yan sa kan sun zata ɓata gari ne a motar da suka tare.