Saudiyya Ta Ba Ɗaliban Najeriya 50 Guraben Karatu A Fannin Man Fetur Da Ma’adinai
Masarautar Saudiyya ta ba wa ɗaliban Najeriya 50 guraben karatu cikakku a fannonin albarkatun man fetur da ma’adinai. Jakadan Saudiyya a Najeriya, Yousef Bin Mohammed Al-Balawi, ya bayyana cewa shirin guraben karatun ya haɗa da kuɗin makaranta, tikitin tafiya, masauki da kuma alawus na wata-wata a Jami’ar Man Fetur da Ma’adinai ta Sarki Fahd. Jakada […]