139
A jiya Litinin ne babban layin dake samar da wuta ga Jihohin Arewacin Najeriya na sake ɗaukewa.
Bayanin sake ɗaukewar layin wutar na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Babbar Manajan Hulɗa da Jama’a ta Kamfanin Raba Wutar Lantarki na Najeriya, Ndidi Mbah ta fitar a safiyar Talata.
A cikin makonni biyu, wannan shine karo na shida da babban layin wutar ke lalacewa .