Home » Za A Yi Zaben Kananan Hukumomi Ranar Asabar-Majalisar Kano

Za A Yi Zaben Kananan Hukumomi Ranar Asabar-Majalisar Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ce babu fashi dangane da gudanar zaɓen ƙananan hukumomin jihar da ke tafe ranar Asabar mai zuwa.

Majalisar ta jaddada cewa babu abin da zai hana a gudanar da zaben ƙananan hukumomin kamar yadda aka tsara a ranar Asabar 26 ga watan Oktoba, 2024, duk da hukuncin Babbar Kotun Tarayya na soke Hukumar Zaɓe ta Jihar Kano (KANSIEC).

A ranar Talata 22 ga Oktoba, 2024 ne dai mai shari’a Simon Amobeda na Babbar Kotun Tarayya ya ba da umarnin rushe shugabancin hukumar zaɓen jihar Kano, bisa dogaro da hujjojin da aka gabatar na rashin cancantar shugabannin.

Mai Shari’a Simon Amobeda ya yanke hukunce-hukunce 10 dangane da hukumar zaben jihar Kano. 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?