Ma’aikatan VOA Sun Maka Shugaba Trump A Kotu
Wasu daga cikin ma’aikatan kafar yaɗa labaran Muryar Amurka (VOA), sun maka shugaba Donald Trump, a gaban Kotu bisa zargin sa da rufe kafar yaɗa labaran ba bisa ƙa’ida ba.
Wasu daga cikin ma’aikatan kafar yaɗa labaran Muryar Amurka (VOA), sun maka shugaba Donald Trump, a gaban Kotu bisa zargin sa da rufe kafar yaɗa labaran ba bisa ƙa’ida ba.
Rahotanni na cewa sojojin Sudan a ranar Asabar sun kwace wasu muhimman gine-gine a tsakiyar birnin Khartoum, ciki har da babban bankin kasar daga hannun dakarun Rapid Support Forces (RSF), bayan sake ƙwace fadar shugaban kasar.
Jaridar TRT Hausa ta bayyana cewa Gidan talbijin na Sudan ranar Alhamis ya ce sojojin ƙasar na dab da karɓe iko da Fadar shugaban ƙasar a Khartoum daga hannun dakarun rundunar RSF, lamarin da ya kawo wani babban sauyi a yaƙin da aka yi shekara biyu ana gwabzawa wanda yake barazanar raba ƙasar.
Kungiyar ‘yan tawayen M23 ta ce hare-haren da Kwango ke kaiwa kan jama’a na nuna DRC ba ta damu da a tattauna a Angola ba.
Daga Shareef Khalifa Sharifai Mayakan M23 sun kai sumame asibitin CBCA da asibitin Heal Africa a daren Ranar 28 ga watan Fabrairu, inda suka yi awon gaba da marasa lafiya 116 da wasu 15, A cewar mai Magana da yawun ofishin kare hakkin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, Ravina Shamdasani. Ana kyautata zaton mazajen […]
Ƙasar Isra’ila na ci gaba da shan suka mai zafi daga bangarori daban-daban na duniya bayan sanar da katse duk nau’in tallafi daga shiga zirin Gaza.
Ofishin Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya amince da bukatar Amurka na tsawaita wa’adin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni har zuwa bayan azumin Ramadan.
A watan Satumba na shekarar da ta gabata ta 2024 gidan talabijin da rediyo na Muhasa dake a kasar Najeriya ya kai ziyarar aiki zuwa sassan jamhuriyar kasar Nijar. Jihar Maradi na daya daga cikin jihoshin kasar ta Nijar kuma ita ake yiwa lakabi da cibiyar kasuwanci ta kasar Nijar, wannan gidan talabijin na Muhasa […]
Asusun Tallafa Wa Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya ce bai wa yara abinci mai gina jiki cikin kwanakin dubu 1000 na farko bayan haihuwarsu na taimakawa matuƙa wajen bunƙasar ƙwaƙwalwa da haɓakar giraman jikinsu. Jami’ar kula da ingantaccen abinci kuma wakiliyar UNICEF a Kano, Abigail Nyam, ce ta bayyana hakan a ranar […]
Wani rahoto da Hukumar ƙididdiga ta ƙasar Argentina ta fitar na nuni da cewa rabin mutanen ƙasar na fama da matsanancin Talauci. Wannan na bayyana cewa an sami ƙaruwar talauci da kaso 40% cikin 100% na shekarar da ta gabata, kuma ya nuna tasirin matakan tsuke bakin aljihu da gwamnatin shugaban Ƙasar Javier Millei ta […]