Babban Labari

An Gudanar Da Jana’izar Alhaji Aminu Ɗantata A Birnin Madina

An gudanar da jana’izar hamshaƙin ɗankasuwar nan na Najeriya, Marigayi Alhaji Aminu Ɗantata a masallacin Annabi (S.A.W) da ke birnin Madina. Jana’izar ta gudana ne bayan sallar magariba, inda kuma aka binne gawarsa a maƙabarta Baƙiyya mai tarihi a birnin na Madina. Mutane da dama ne daga Najeriya suka halarci jana’izar – wadda aka jinkirta […]

Read more

Gwamnan Bauchi Zai Kirƙiro Sabbin Masarautu

Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi ya amince da kafa kwamitin mambobi 41 da nufin kafa sabbin masarautu a faɗin jihar. Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar ta bayyana cewa kwamitin ya ƙunshi fitattun mambobi 41 da aka zabo daga ɓangarori daban-daban, ciki har da sarakunan gargajiya, ƙwararru, malaman jami’a, wakilan ƙungiyoyin […]

Read more

Dangote Ya Kara Rage Farashin Man Fetur.

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur daga naira 880 zuwa naira 840 ga dillalan da ke siyan man daga matatarsa, a wani mataki da ya zo gabanin fara rabon man a faɗin ƙasa daga 15 ga watan Agusta. Shugaban hulɗa da jama’a na matatar, Anthony Chiejina, ne ya bayyana hakan, yana mai […]

Read more

Wani Dan Fashi Ya Mutu Bayan An Yi Masa Duka A Kano

  Rundunar yan sandan jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar wani matashi mai suna Musa Nuhu, mazaunin unguwar Dorayi Jakada, bayan Yasha dukan kawo wuka lokacin da ake zargin yaje wani gida yin fashi da makami. Kakakin rundunar yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da […]

Read more

An Dage Jana’izar Aminu Ɗantata Zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana’izar fitaccen ɗankasuwar nan, Alhaji Aminu Dantata da ya rasu ranar Asabar a ƙasar Hadaɗɗiyar Daular Larabawa. Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya tabbatar wa da BBC ɗage jana’izar sakamakon rashin isar gawar marigayin a kan lokaci zuwa birnin Madina. ”Akwai ƙa’idoji da gwamnatin Saudiyya ta shimfiɗa kan […]

Read more

Iran Ta Ci Gaba Da Aikin Nukiliyarta

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da inganta sinadarin Uranium, mako guda bayan da Amurka ta haɗa hannu da Isra’ila wajen kai harin bama-bamai a manyan cibiyoyin nukiliyarta. Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar Majid Takht-Ravanchi ya shaida wa BBC cewa za a iya tattauna iya matakin da za a iya kai wa na […]

Read more

Jana’izar Aminu Ɗantata: Abba Da Sarki Sanusi Sun Tafi Saudiyya

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, tare da Gwamnan Jigawa, Umar Namadi da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, sun tafi ƙasar Saudiyya domin halartar jana’izar Alhaji Aminu Ɗantata. Gwamnan ya jagoranci tafiyar ce domin halarta Sallar Jana’izar a Madina ne, bayan rasuwar hamshaƙin attajirin a birnin Dubai da ke ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa a […]

Read more