Mutane 12 ne suka rasu sakamakon hadarin mota daya auku da safiyyar yau juma’a a kauyen samawa dake karamar hukumar Garun Malam.
Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa dake nan Kano ya bayyana cewa hadarin ya rutsa da wata mota kirar DAF.
Yace motar tana dauke ne da kayayyaki dabam dabam na amfanin yau da kullum.
Haka kuma motar tana dauke da fasinjoji.
- Masu Ruwa Da Tsaki A Unguwar Sharada Sun Amince Da Dokoki 29 Don Gyara Tarbiya.
- Wata Kotu A Canada Ta Aiyana APC Da PDP A Matsayin Kungiyoyin Ta’addanci
Mai magana da yawun hukumar Abdullahi Labaran ya bayyana cewa mutane 19 ne hadarin ya rutsa dasu inda mutane 12 suka mutu nan take kuma an kai gawawwakin asibitin Nasarawa yayinda kuma sauran da sukaji ciwo ake kulawa dasu a asibitin Garin Kura.
Ya ce hadarin ya faru ne bayan da tirelar ta kwace daga hannun direban.