Rundunar yan sandan jihar Kano, bisa jagorancin kwamishinan ta CP Ibrahim Adamu Bakori, ta karawa jami’anta biyu girma , a matakai dabam-daban.
An gudanar da taron Karin girman a wajen shakatawa na manyan jami’an yan sanda dake unguwar Bompai Kano.
Kwamishinan yan sandan, ya bukaci yan sandan da suka sami karin girman, y ace wannan ya zama babban kalubale a garesu wajen kara jan damarar yaki da masu aikata laifuka a Kano dan samun zaman lafiya.
- DSS Ta Bankado Yadda Kwamishina Namadi Ya Karbi Dala $30,000 Don Ya Karbi Belin Dilan Kwaya.
- INEC Ta Saka Ranar Fara Rajistar Masu Zaɓe A Faɗin Najeriya
CP Bakori ya jaddada kudurin rundunar yan sandan Kano na wanzar da zaman lafiya da kare dukiyar al’ummar baki daya.
Wasu daga cikin ‘yan sandan da aka manna musu mukaman nasu na karin girma sun bayyana farin cikin su akan wannan ci gaba da suka samu.