Dakarun gwamnatin kasar Sudan da ta RSF sun kulla yarjejeniyar tsagaita wuta saboda babbar sallah

A yau ne yarjejeniyar tsagaita wuta da shugaban rundunar dakarun RSF ya sanar za ta fara aiki domin bukukuwan babbar sallar Idi da za a fara ranar Laraba.

An bayar da sanarwar dakatar da rikicin ne a wani sakon murya da aka watsa a gidan talabijin, wanda shugaban kungiyar RSF, Muhammad Hamdan Dagalo, ya gabatar.

Ya ce matakin zai yi aiki ne a ranakun Talata da Laraba.

Janar Hemedti ya kuma yi Allah-wadai da cin zarafi da ake yi wa fararen hula – ciki har da wadanda sojojinsa ke yi.

Ana zargin kungiyar ta RSF da aikata laifukan cin zarafin mutane a Darfur.

Post masu alaƙa

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Venezuela ta sanar da ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.