Dakarun sojin Ofureshin Hadarin Daji sun kashe ‘yan bindiga 10 da ceto wasu da dama

Dakarun sojojin ‘Operation Hadarin Daji’ a jihar Zamfara sun halaka ƴan bindiga 10 tare da ceto wasu mutum tara da aka yi garkuwa da su.

Hakan na cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙsa ta wallafa a shafinta na Twitter, inda ta bayyana cewa, ƴan bindigan sun taho ne daga jihar Sokoto ta hanyar ƙauyen Gadazaima a jihar Zamfara.

Post masu alaƙa

Gidauniyar “Renewed Hope” Ta Tallafa Wa Gidaje Marasa Galihu 154,412 A Jigawa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga