EFCC Ta Aiyana Timipre Sylva A Matsayin Wanda Take Nema

Hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da Rashawa a Najeriya ta ayyana neman tsohon gwamnan jihar Bayelsa, Timipre Sylva ruwa a jallo.

Cikin wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na X ta ce tana neman Mista Sylva ne bisa zargin wata badaƙalar kuɗi da yawansu ya kai dala miliyan 14.8.

EFCC ta zargi tsohon gwamnan ne da karkatar da kuɗin da aka yi niyyar amfani da su wajen gina matatar man fetur a ƙasar.

Hukumar ta ce wata kotu ce a jihar Legas ta bayar da sammacin kama tsohon ƙaramin ministan na man fetur na Najeriya.

Hukumar yaki da cin hancin ta kuma buƙaci duk wanda yake da bayanan da za su taimaka wajen kama tsohon gwamnan ya gabatar mata da su.

Post masu alaƙa

Tinubu Ya Sha Alwashin Ceto Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Oyo Da Borno

Kwamishinan ƴan sandan Kano, CP I.A. Bakori ya gargaɗi dakarunsa su guji shiga harkokin siyasa.

Alhazan Kebbi Rukunin Farko Sun Dawo Gida