FRSC ta tabbatar da mutuwar ɗaliban jami’ar Jos 8 a haɗarin mota

Hukumar kiyaye haɗurra ta Najeriya, FRSC a jihar Filato ta tabbatar da mutuwar daliban jami’ar Jos takwas sakamakon wani mummunan hadarin mota da ya ritsa da su.

Hadarin dai ya auku ne da misalin karfe biyu na dare a akan titin zuwa Zaria a birnin Jos inda wasu da dama suka jikkata.

FRSC ta ce hadarin ya faru ne yayin da motar da ɗaliban ke ciki ta yi taho-mu-gama da wata motar kaya, lamarin da ya janyo mummunan lahani.

Rahotanni sun ce ɗaliban na kan hanyarsu ta komawa ɗakunan kwanansu bayan fitowa daga shaƙatawar dare lokacin da abin ya faru.

Ana dai cigaba da kula da wasu ɗalibai biyu da suka tsira daga hatsarin bayan an garzaya da su zuwa wani asibiti mafi kusa domin samun kulawar gaggawa.

FRSC ta ce an fara bincike don gano ainihin musabbabin faruwar wannan mummunan haɗari, tare da kira ga direbobi da su rika tuki cikin natsuwa musamman a lokutan dare domin guje wa irin haka.

Post masu alaƙa

Kwankwaso da Dickson sun gana kan rikicin NDC a Kano

An gurfanar da mutane 24 kan zargin kashe Ummulkhairi a Mararrabar Jos, Kaduna

Sojoji sun ceto mutane 47 da ISWAP ta yi garkuwa da su a Borno