Hukumar Kula da Hanyoyi ta Najeriya FRSC ta sanar cewa ta inganta cibiyar buga takardunta don samar da matsakaicin lasisin tuƙi guda 15,000 a kowace rana wanda hakan zai bayar da damar karɓar lasisin tuƙi nan take.
Wannan mataki na da nufin kawar da dukkan jinkirin da ake samu wajen karɓar lasisin tuƙin wajen ƙoƙarin ganin sun sallami duk masu neman ayi musu lasisin tuƙi kafin nan da tsakiyar watan Nuwamba
Kwamandan FRSC, Shehu Mohammed ne ya bayyana haka a Abuja bayan ziyartar cibiyar buga takardun, inda ya ce sabon tsarin zai magance matsalolin jinkirin da ake samu wajen sarrafa lasisin direba da lambobin motoci, kamar yadda jaridar Gaurdian ta ruwaito.
Mohammed ya ce FRSC zai fara amfani da tsarin ɗaukar bayanan yatsu hannun mutum daga nesa tare da buga lasisin nan take wanda zai kawar da lasisin wucin gadi.
Ya kara da cewa wannan ci gaba zai sa jinkiri da sauran matsalolin da suka shafi lasisin tuƙi na ƙasa su zama tarihi.