Home » FRSC Za Ta Fara Bayar Da Lasisin Tuƙi Nan Take

FRSC Za Ta Fara Bayar Da Lasisin Tuƙi Nan Take

Hukumar Kula da Hanyoyi ta Najeriya FRSC ta sanar cewa ta inganta cibiyar buga takardunta don samar da matsakaicin lasisin tuƙi guda 15,000 a

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Hukumar Kula da Hanyoyi ta Najeriya FRSC ta sanar cewa ta inganta cibiyar buga takardunta don samar da matsakaicin lasisin tuƙi guda 15,000 a kowace rana wanda hakan zai bayar da damar karɓar lasisin tuƙi nan take.

Wannan mataki na da nufin kawar da dukkan jinkirin da ake samu wajen karɓar lasisin tuƙin wajen ƙoƙarin ganin sun sallami duk masu neman ayi musu lasisin tuƙi kafin nan da tsakiyar watan Nuwamba

Kwamandan FRSC, Shehu Mohammed ne ya bayyana haka a Abuja bayan ziyartar cibiyar buga takardun, inda ya ce sabon tsarin zai magance matsalolin jinkirin da ake samu wajen sarrafa lasisin direba da lambobin motoci, kamar yadda jaridar Gaurdian ta ruwaito.

Mohammed ya ce FRSC zai fara amfani da tsarin ɗaukar bayanan yatsu hannun mutum daga nesa tare da buga lasisin nan take wanda zai kawar da lasisin wucin gadi.

Ya kara da cewa wannan ci gaba zai sa jinkiri da sauran matsalolin da suka shafi lasisin tuƙi na ƙasa su zama tarihi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?